Inna Lillahi wa Inna Ilaihi rajiun Dan Allah iyaye idan yaranku sun kawo muku qarar miji ku dinga yi musu sulhu ku dena korar yaranku ko gwalesu, idan abu ya gagara a raba auren Ku kuma mata ku dena daukko wuqa duk azabar da namiji ze muku, gwanda ku fita ku bar masa gidan akan daukko wuqa, ku kuma maza ku ji tsoron Allah da rage zafin zuciya da zalincin tauyewa mata hakki abin yayi yawa fa Allah ya rabamu da sharrin hawa dokin zuciya Amin Mallam dan Allah ku dinga yiwa iyaye waazi akan su dena korar yaransu mata su dinga sauraransu dan Allah suna bincikawa, dan wallahi rana zafi inuwa quna hk muke mata ba inda zk kaji dadi sai de wajen mahaliccinka Allah
Gaskiya you make a very crucial point Don Allah iyayen ku dinga sauraron yar ku idan ta kawo karar mijinta ku daina korar su da gwalewa. Allah yasa mudace
Gaskiya ka yi magana mai kyau a nan. Ba kaman Abu Aisha na alfurqan ba. Shi kawai zuwa ya yi ya daura laifin a kan matan ba tare da jin bangarori daban ba. Wannan kuma rashin adalci ne. Allah ya rufa mana asiri ya gyara mana zuriar mu.
Bana goyon bayan kisan datayi masa ya sheikh....Amma indai abubuwan data fada yana yimata gaskiya ne shi yajawa kansa. Babu abinci ga duka. Taje gida ta fada ankorota iyayema da laifinsu
@sakinadeeni4713 Wallahi kuwa, da wanne zataji....babu abinci, ba magana mai kyau, ga dukan tsiya ga jego.....Gashi kuma taje gidansu an korota....Haba ! Toh ya Ilahi ina zatasa kanta? Ita a ganinta yin hakan shine mafita agareta. Natausaya mata matuka...Dafatan za'ayi mata sassauci wurin hukunci
Ai daga dukan ne Shaidan yake haddasa kisan, abinda ze janyo kisa maza zasu dena gsky, mata ku kuma duk azabar namiji gwanda ku fice ku bar masa gidan yafi sauqi akan daukar wuqa. Allah ya rabamu da mummunar qaddara Maza kuma ku dena kisan alumar Annabi yanzu duk yaqin duniya da sauran kashe kashe waye yake ba maza ba, kai de kawai Allah ya shirya kowa Amin
Hausawa kunci amanan addinin Allah wallahi. Da manyanku da yaranku akwai matsalan rashin tarbiyya wallahi. Ina amfanin zuwa islamiyya kullun? Allah ya shirya.
Wanan yarinyar postpartum depression ne wallahi ke damun ta...maza idan mata suka haihu akwai mental distress da ke damun wasu saboda trauma na haihuwa
Malam Allah ya saka da alkhairi. Maganar ka haka take. Allah ya raba mu da mummunar qaddara😭. Gsky batayi kama dame iya kashe kaza bama, bare mutum. Qaddarar tace tazo a haka. Kuma bawai ina goyen bayanta bane ko abun da tayi daidai ne. Amma ya kamata a cigaba da fadakar da maza masu dukan matansu. Allah yasa mu dace ya tsare mu ya tsare imanin mu
Bai kamata aki taimaka mishi ba wlh. Wannan furucin na kin taba shi ya tsayar mata arai Abu ne da bazata tana matawa ba, Allah ya rabamu da mummunar kaddara, ya kawo mata mafita
Gaskiya malam. Sannan a wayarwa da iyaye kai in yarinya tazo gida da damuwa aki me zata fada a kiraijin ma aji daga gareshi, amma iyayenmu sai suce aure dn hakuri ne kowa hakuri yake wasu ma ko sauraron me kazo dashi basa yi, gaskiya ya kamata a gyara jazakalla khairan
Wai shin ilimin da Malam yakoya yakarene mukaga yakoma kallon social media Yana tsokaci ?? Mufa haryanzu munada bukatar ilimunmuka na addini ne bawai labaran midiyaba
Don Allah jahilan maza kudena goyawa iron wayan wayannan mata kowa yaganta baiga Mai yunwaba mara kunyace tace gida baa goyon bakanta kariya take wa yasani metake masa bawahala ajikinta in har sai makota sun Bata abinci da alalace take mata sun zama mahautan mazan su subhanallah