Dan Allah yan Nigerya kadada kuyi zanga zanga, talauci da kuncin rayiwa ba garaiku farauba. Mu à Niger ba irin halin da bamu shigaba amma mu kayi hakuri. Dan Allah yan nigeria kuyi hakuri. Kuma mu yan Niger muna rokon Allah ya kawo muku sauqi. Ku ji tausayin tallakawan ku. Bama fatan a qara samun yan gudun hijira.
Mallam ka fadi gaskiya ka bar son rai,da kake cewa Hausa da Fulani daya ake.Duk arewancin Nigeria Babu ko bahause guda Wanda ake jí dashi illa Fulani kadai ne mi yasa haka in ba kabilanci irin naku ba
Illolin zanga zanga. 1. Babu alheri a ciki kamar yadda ba alheri a wannan mulkin. 2. Zaa rufe shaguna kasuwanci ya tsaya chak, kamar yadda tsananin tsada da rashin kudi ya tsayar da kasuwanci chak a yanzu. 3. Zaa balle shaguna a kwashe kaya, kamar yadda samari suke balle shaguna a yanzu. 4. Zaa kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba, kamar dai yadda yan taada ke sace mutanen da basu ji basu gani ba su kashe a yanzu. Shin wai menene banbanchin rayuwa a nigeria yau da kasar da ake yaki? Burodi ya fi araha a libya da Syria akan nigeria. Tsaro a Libya, Sudan da Syria yafi na Nigeria a yanzu. Ya kamata mu sani yin zanga zanca na iya sa shugabanni su shiga taitayinsu. Ko ba komai idan rumfar da duk muke ciki ta rikito kowa ya dawo dai dai da kowa ai an yi nasara. Sai kawai a sake zuba wasa wannan karon talaka sa ido a yadda wasan zai kasance kamar dai abinda ya faru a Kenya.