Mun gode da ka nuna mana adireshin ka. Dama kowa ana gane shi waye daga maganar sa. Amma abinda zan fada maka shine har a gaban Allah sai an mana hisabi kan wannan zagi da ka yi mana. Zaka fada wa Allah cewa mu tsinannu ne ko a'a. Zaka biya mu hakkin wannan zagi a kotun da ba'a zalunci. Gaban alkalin da ba'a bashi cin hanci, balle ya juya hukunci. Don haka ka shirya wa wannan case. Ka Tanadi amsar da zaka gamsar da Allah cewa mun cancanci tsinuwa.