Malam Allah ya saka da Alkhairi nima ina da tambaya bayan na shekara biyar zuwa shida a gaban mahaifiya ta sai na koma gaban kanwar kakata sai da na shekara goma zuwa sha daya sai na qara komawa wajen mahaifiyata to yanzu maganar da nake malam ni budurwa ce kuma ina sana'a ina samu Alhamdulillah ina so inyi wa qanwar kakan nan tawa alkhairi sai nake ganin kamar ran mahaifiyata yana baci to ni kuma sai na bari amma dai ina da burin yi mata shine nake so malam kayimin bayani naji kuna cewa haqqin uwa yafi na kowa akanka a duniya to ita maman nawa ina mata ba laifi amma malam ina so inyi wa kanwar kakar tawa da yayanta duka amma bana so ran mahaifiya ta ya baci saboda Allah yace mu kyautata mata Allah yasa saqona ya isa wurin malam nagode.
Zaki iya kyautatawa kanwar kakanki ai batare ta mahaifiyarki tasani ba. Ki kyutata niyar ki kawai kuma ki kula da mahaifiyarki fiye da kowa saboda tafi kowa hakki a kanki. Bayan nan ki sani shi kyauta ko sadaka Allah ne ya halattashi kuma ya umurci mu muyi kuma halal ne baya kan hurumin iyaye balle su hanaki yi, amma Zaki iya boyewa saboda zaman lafiya da iyayenki. Amma ki taimaki kanwar kankanki saboda itama tabada gudumawa wajen tarbiyanki da rayuwanki. Wallahu Ahlam