...Assalamualaikum Warahmatullahi Wabarkatuhu,Da Farko Hajiya Madina Dole A Yaba Da Kokarin Ki Wajen Binciko Maodu'ai Masu Muhimmanci A Rayuwar Mu Ta Yau Da Kullum.Amma A Zahirin Gaskiya Ba'ayima Wannan Maudu'an Adalcin Da Ya Dace Wajen Kawo Mutanen Da Zasuyi Fashin Baki Akan Su,A Bunda Nake Nufi Shine,Tunda Kuka Fara Wannan Shiri Daga Farkon Sa Har Zuwa Yau Wallahi Bai Taba Wuce Ni Ba.Da Yawa Daga Maudu'an Da Kuke Dakkowa Abune Da Malaman Musulunci Ya Kamata Ku Dinga Gayyatowa Tunda Kuna Da Damaryin Hakan Saikiga Ana Samun Abunda Ya Dace Sosai Wajen Fadin Hakkokin Allah Da Manzon Sa Akan Wannan Maudu'an Amma Sai Kukeyin Amfani Da Mutanen Da A Zaton Ku Sun Shahara A Social Media Kuce Zasuyima Wannan Maudu'an Adalci Kuma Wallahi Saisu Gagara.Shawara Na Anan Shine Inhar Maudu'in Da Zaku Tattauna Yashafi Addini Kai Tsaye To Abawa Wannan Maudu'in Hakkin Sa Wajen Gayyato Malaman Addini Maza Ko Mata.A Malaman Mu Maza Akwai Irin Su Dr.Basheer Aliyu Umar, Sheikh Abdallah Gadon Kaya, Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah, Sheikh Amini Ibrahim Daurawa Da Sheikh Muhammad Kabeer Haruna Gombe...A Mata Akwai Irin Su Malama Zainab Ja'afar Mahmood Adam, Malama Zuwairiyya Bauchi Da Malama Zainab Aliyu Gombe...Amma Ina Fata Za'amin Kyakykyawan Fahimta.Hausawa Suna Cewa Gyara Kayan Ka Bai Zama Sauke Mu Raba Ba...Daga Naku Har Kullum Elyaseen Dauda Elyaseen (Elyaseen Kumby)08037599091.
Wallahi gaskiya ka fada. Amma ni abun dana fahimta shine: BBC Hausa suna yin program dinne don nishadantar da masu kallo ba don kawo gyara ba. Domin idan har suna yi ne don kawo gyara da samun chanji toh kuwa tabbas zasu dinga gayyato Malamai Masana (maza ko mata). Amma mafi akasarin wadanda ake gayyatowa en boko neh da matasan da suka shahara a social media suna fadawa mutane tunaninsu ba abun da Allah (SWT) da ManzonSa (SAW) suka ceh bah. Shi kuma addini koh Shari'ah ba tunani bane face ilimi.
Honestly su neman kudi suke sannan kuma daman baya cikin ƙa'idar aikin su yin gyara a addini. Misali ita tashar holders din ta turawan biritania ne wanda su kuma ba addini ne damuwa suba rayuwa yau da kullum itace gabansu
Shi fa qarin auren nan Allah ne Ya halitta shi, in dai har namiji zai kwatanta adalci mu kuma matan mu tsarkake zuciyar to gaskiya kishi bazai samu wuri a gidan ba.
Wato gaskiya akwai matan da ko rayuwar ka zaka basu bazaku zauna lafiya ba saidai in kayi musu kishiya zasu gane kuskurensu daga baya su dawo suna danasani, Allah yasa mu dace
Mafi yawancin mazajen da suke Kara aure su bukatar su kawai suke dubawa basa duba Bukatuwar matan akan abinda karin auren zai haifar, maza su damuwar su kawai suke dubawa Unfortunately.
Kishi kumalun Mata... Allah yabamu kishiyata konace abokiyar zama tagari.. nidai Ina bawa kowacce mace hakuri kutina Allah ne yabasu dama suyi daga 2,3,zuwa 4.. so bayacce zaamuyi idan min yarda da haka wlh bbu wani Abu da zai daga miki hankali.. nabiyu idan zaai Miki kishiya ki ninninka biyayyarki da kulawar dakike bashi kinemi aljannarki bbu ruwanki da sa kishiyarki arai wlh kisani mijinki aljannarki ne... Amma Wani abin takici sai kiga mace anmata kishiya ta burkice tana ta abin yara.. Allah yasa my dace... Ku kuma maza ku Dunga kwatanta adalci wlh karkayi aure kadunga wulakanta matarka ta farko.. ko idan ka gama da wancar amaryar shnkn tazama yar gida sai wulakanci kasani wlh duk abinda Kai sai anyi wa yarka sannan manzo saw yace kullukum ra'in wakullukum masulu arra'iyatihim... Dukkaniku makiwatani Kuma zaa tambayiku abisa kiwon daaka Baku... Akiyaye Dan Allah adunga adalci... Ngd
Dr da hajiya sunyi bayanai masu ma'ana akan matsalolin kishiyoyi amma karin akan banan shine barin faɗar akan abokiyar zama ba kiahiya and ƙazanta wasu matanma tana sawa karo aure, mace zata office tayi wanka kamar zata karɓan tiket na aljanna amma intana gida kamar mahaukaciya a bola
Asalamu alaikum malama Madina Allah ya saka muku da alkhairi game da fadakarwar da kuke na wanan shirin.Ni dai a nawa abunda ya sa wasu mazajen in zasu kara aure basa sanar da iyalin su nagida shine dan gudun kar ta baci,kamar ita matar tagida ta shiga tsananin damuwa,watama har hakan zai iya sanya ta ta bar hanya(Boka,Stibace stibace,DSS),musaman ma in matar ta kasance mai yawa bin maganganu kawaye,wasu kuma iyayen su ne mata ketura su dan ganin hana ruwa gudu.Allah ya sa mu dace.
maganan Dr gaskiya abunda yesa nace hakan Maza haka Allah yayi su inda zasu iya Kara aure fiye da 4 ma da sunkara indadin sukeji sai suche barin karawa kaina dadin in babu dadinma suche barin nemawa Kaina mafita kawai mata zaman hakuri zakuyi da zaman aure ibada ne kisawa ranki hakan Allah yebamaa masu auren zaman lafiya mu mata Allah yebamu mazaje nagari Wanda yasan mutunchi mace Kuma yasan mene auren daga Fatima mustapha a jahar Borno
Abubuwanda doctor yayi mentioning they are all true as well the other lady.. but the main problem din, is from the male side, Gaskiya maza Baza Iya hakurin fahimtar Matansu GameDa Karin Aure. Idan Namiji yanada Bukatan Karin Aure seya duba wasu Dalilai ne zesa ya Kara auren. Sun Kai yayi koko. Firstly, Financially, sexually... but, Maza basa Duba wadannan
Duk wani matsala azaman takewar Aure mu maza muke haddasa shi, Because idan kanada mata 2 kayi adalci, Karka fifita amaryan ka akan uwar gidanka, Kaikeda wuka da nama kaine keda hakkin yin adalci ga kowa.
Anty madins barka da aiki. Muna jindadin shirin nan sosai. Inda hali a kara mana zuwan shirin nan sau 4 a wata. Saannan gaskiya mic dinki baya picking sound da kyau kamar yanda na guest dinki yake fitowa clear. Nagode.